Thursday, October 29, 2020

MAFARKINAH JIYA DA DADDARE

 




 ( MAFARKINAH JIYA DA DADDARE)💞
Ku biyoni kusha Labari
💞💓💞

Annabi S.A.W Ya-ce " Mafarki Mai kyau daga Allah ne..
...Mafarki Mara kyau daga shaiɗan ne..

Malamai sunyi ƙarin bayani Game da mafarki Mai kyau .. zaka iya bayyanawa..
Mafarki mara kyau kuma idan kayi ka nemi tsari daga shaiɗan kayi tofi sau uku.. kuma mutum ya ka-me bakinsa basai ya bayyana ba..

Alhamdulillah 🙏😍
Sabda Wannan Dalilin ne ,nakeso bayyana mafarkin danayi daren jiya.
.
Tare da wata baiwar Allah,wacce friend dita ce.. tsawon shekaru da dama a wannan kafa ta Sa-da zumunta...
Ban taɓa ganinta ido-da ido ba,..

WALLAHI BAN SANTA DA WANI AIKI BA, FA-CE AYYUKAN ALKHAIRI A WANNAN KAFA TA FACEBOOK SOSAI,WAJEN DA'AWA ,FAƊAKARWA ..
ALLAH YASAKA MATA DA ALKHAIRI.

Allah cikin ikon sa,Ƙudirar sa.., jiya nayi Mafarki da ita Malama Faridah Bintu Salis ,😍

Na Gammu acikin wani babban masallaci.., Masallacin yayi kama da masallacin juma'a, Muntara Mata dayawa Bila adadin .., masallacin yacika MaQil da Mata..

Mu kuma muna kan wasu kujeru a saman step.. ko wacce da Alarammiyyar ta, Nafara tafsirin Alkur'ani Mai Girma acikin سورة عبس
🎤🎤🎤

Alarammiyya ta wacce bansan ko wacece ba a mafarkin tana jaa min BaQee Ni kuma ina FASSARAWA... Idan nayi nagaji sai Malama #Faridah_Bintu_Salis ta ƙarɓa taci gaba da tafsirin Ana jaa mata baQee ..🎤🎤
Mata na sauraren tafseerin Alkur'ani mai Girma daga bakunan mu..🎤🎤🎤

Agefe kuma wani Malamin Islamiyyar mu ne a Zamfara..
Malam Muhammad Sani Abdulkarim Gusau.
Shugaban makarantar مدرسة تربية الإسلام تدون ودا غسو.

Shiyake Guiding din mu idan wata kalma ,fassarar ta tashige mana yafassara mana..

Ana cikin haka Ina tafseerin sai wasu kalmomi suka shige mun , namanta fassarar su..
Kalmar عبد
(Abdu)

Da kuma عربا
(Urbaa)

Sai na tambayi Malama #Faridah fassarar su sai tace wallahi Malama nima fassara ta shige mun...

Sai na tambayi wannan malamin namu na Islamiyyah ,Sai Ya tuna mana fassarar kalmomin ,muka ci gaba da tafseerin Abun mu..
😍
Anan Nafarka da Dadda ɗan Mafarkinah na daren jiya..
Around 2:10am Na dare...
Wallahi sabda farin ciki nakasa komawa barci,ina ta tasbihi ga Allah, Na dauki tsawon lokaci kafin wani baccin Ya daukeni..

Alhamdulillah 🙏
Allah nake Roko Ya tabbatar da wannan Mafarkin nawa..

Annabi S.A.W Yace"Mafi Alkhairin ku,Wanda Ya koyi ALKUR'ANI KUMA YA KOYAR DASHI."

Yaa! Ka bamu ilimin wannan littafin naka,
Mu amfanar da Al'umma dashi..
YAa HAYYU Yaa QAYYUM.

Dukkanin wani ko wata da Take da babban Buri akan Littafin ka Mai Tsarki..
Allah ka sauƙaƙe mana hanyar koyon shi ,Muhaddaceshi,Mu amfanar da Al'umma dashi..

YAa HAYYU Yaa QAYYUM 🤲
Allah kasanYa Alƙur'ani yacecemu Ranar Gobe kiyama.

Ina miki Fatan Alkhairi.
Malama #Farida_Bintu_Salis

Safeeyyah Suleiman Umar
25-Oct.2020.

SHEIK ALBANY (RAHIMAHULLAH)


 

Sunana Muhammad Auwal
Sunan Mahaifina Adam
Sunan mahifiyata Saudah
Abu - Abdirrahman shine Alkunyana
Albaniy shine Lakabina
An haifeni a Anguwan Muciya Sabon Garin
Zaria a shekarar 1960
Nayi makarantar Allo har nayi sauka
Na koyi littafan da akeyi a zaure na fiqhu
dana lugah da Adab
Nayi karatu a wurin manyan malamai
mabanbanta a kasata Najeriya da kasashen
waje inda na koyi Qur'ani da dukkan
kira'o'insa, Hadisi da musdalah dinsa, Tafsiri
da Usul dinsa, Tareekh da usul dinsa,
Aqeedah da Manhaj da usul dinsu, Harshen
larabci da fannoninsa, Fiqh da Usul da
Qawa'id dinsa, d.s
Nayi makarantar firamare a Sabon Garin
Zaria
Nayi Sakandire a kwalejin Barewa Zaria
Nayi Diploma akan:
Law
Computer Science
Mass Communication
Hausa Language
Nayi Degree akan ICT
Nayi Masters akan Islamic Studies
Ni Professional Jounalist ne
Ni Certified Microsoft Engineer ne
Ni Linguistic ne
Na karanci Library Science
Nayi Programme na N+ akan Computer
Nayi Programme na A+ d.s
Inada Company wanda ke gabatar da ayuka
a fannoni daban-daban
Na karantar da littafai kusan dari a rayuwata
a fagage da fannoni mabanbanta
Na gabatar da Laccoci daban-daban a gida
Najeriya da kasashen ketare
Na fassara littafai na musulunci masu yawa
Nayi Tahqiqin littafai dadama
Na gina cibiya mai suna Daarul-Hadeethis
Salafiyyah Zaria Nigeria(DHSN) wadda a
karkashinta akwai makarantu kamar:
Albaniy Science International Academy(Pre-
Nursery, Nursery, Primary da Secondary) na
bangaren maza dana bangaren mata
Daaru bn Katheer Litahfeezil Qur'an
Sheikh Nasiruddenil Albaniy College of
Higher Islamic Studies
Na fara gina Jami'a mai suna Albaniy
University of Informations and
Communications Technology
Na fara gina gidan marayu
Na samar da inda zan gina Asibiti
Na samar da inda zan gina gidan rediyo da
talbijin
Na samar da dakin karatu(library) domin
anfanar malamai da daliban ilmi
Ni mutum ne mai son cigaban al'ummata ta
hanyar ilmi da wayewa
Manzon Allaah(s.a.w) shine Mai gidana
Banayin sassauci ko 'daga 'kafa akan duk
abunda ya sa'bawa Qur'ani da Sunnah abisa
manhajin magabata na kwarai, amma ina
yin hakan tareda duba yanayi, wuri dakuma
halayen mutane
Daga cikin sana'o'ina akwai:
Dinki
Kanikancin computer(computer engineer)
Mashawarci a harkar computer(Computer
Consultant)
Computer Networking
Aikin Jarida
Kasuwanci maban-banta
Aikin rubuce-rubuce, d.s
Duk abunda na assasa a rayuwata da kudina
na samar dasu, domin ban dogara da kowa
ba bayan Allaah mahaliccina sannan sai
sana'o'in danikeyi

Nayi waqafin abubuwan dana assasa
bakidayansu gareni domin anfanar
al'ummar musulmi
Babban manufata shine sharewa musulmai
hawaye gameda matsalolin dasuke fama
dasu na addini da rayuwa a fannoni daban -
daban a karkashin mahanga na addinin
musulunci

Nasan wadanda suka kasheni da wadanda
sukasa a kasheni, amma KASH! bazai yiwu
indawo duniya in bayyanasu ba! Amma
Ubangijinmu yana nan a madakata yana
jiranmu, a inda ranar Alkiyamah zan shako
wuyansu na gurfanar dasu a gaban Allaah
Sarkin sarakuna ince ya tambayesu dan
meyasa suka kasheni...

Ina rokon Allaah yajikaina

Yayi mini rahma

Ya yafe mini kura - kuraina

Yakarbi shahadata

Ya hadani da mai gidana Manzon Allaah
(s.a.w) a Aljannar Firdausi da sauran
musulmai baki daya. Amin amin amin amin amin amin amin amin amin amin amin amin

AMFANIN KARANTA ALQURANI MAI GIRMA (english version)

 


*Suratul Faatiha* protects one from the anger of *Allah.*

*Surah Yaseen* protects one from the thirst of the Day of Judgment

*Suratul Waaqi'ah* protects one from poverty and starvation.

*Surah Mulk* protects one from the punishment of the grave.

*Suratul Kauthar* protects one from the enmity of the enemy.

*Suratul Kaafiroon* protects one from kufr at the time of death.

*Suratul Ikhlaas* protects one from hypocrisy

*Suratul Falaq* protects one from calamities.

*Suratul Naas* protects one from evil thoughts.

*Advice*
Do not send later. Send it now.
May Allah grant success to every one who reads it and sends it. *Ameen*

#copy

 

ABUBUWAN DA YAKAMATA KIBARI YAYIMIKI KO KICE YAYIMIKI

 


ABUBUWAN DA YAKAMATA KIBARI YAYIMIKI KO KICE YAYIMIKI

1) Kunshi
Ki koya masa yanda ake sa lallai a hannu don wataran yasa miki
Idan kina son nail polish sanda duk kike menses sai ki bashi ya shafa miki.

2) Bashi dankunne ya sa miki. Ko agogo ko awarwaro ko ma sarka.

3) Juya ya zuge miki zif
Sama ko kasa.

4) Inkin wanki kanki, ya bushe. Hada hair oil ki bashi yai miki oiling gashin

5) Bashi mai ya shafa miki a baya. Musamman idan man mai kamshi ne.

6) Ki bari yaga yanda kike kwalliya. Musamman a ina kike sa turare a jikinki.
A wuya, a kasan guiwarki, a hammata,abayan kunne da cibiya. Shafe duk jikinki.
Ki bari ya gani.: Abubuwan da ya kamata
Kuyi tare.

At least sau daya kuyi sallah tare.

1) Kuci abinci tare

2) Ku yiwa juna karatu ko da wani bangare ne a jarida ko dan labari.

3) Cuddle up don yana kara shakuwa.

4)Share your ear piece.
Wani dan peace of wa'azi kika samo ko joke ko ma wata love song.
Sa masa kunne daya, kisa kunne daya kuji tare.

5) Help him shave. Amma don Allah karki yanke shi.
Be very gentle. Show tenderness and love.

6) Yanke masa farce ki bashi foot bath.
Musamman idan a gajiye yake.

7)And jefi jefi don karawa kauna da armashi
Have a pillow fight
Kuyi wasan lido ko snake and ladders.
Duk abinda zai jawo raha da farin ciki a rayuwarku to kuyi.

Ita rayuwa guda daya ce.
In lokaci ya wuce baya dawowa.
Kuma abinda kuka yi shi kuke tunawa.
So me zai hana ku gina abinda in kun tuna zakuji dadi?
: A ko da yaushe su muke mu shiga ran mazajen mu ba mu bari suyi kyamar mu har ju janye jiki ba.
So muke suyi ta doki da alfahari .
Abubuwan da ko kusa karki yarda kiyi su a gaban miji.

1) Tsifar kai. Musamman idan kitson ki yai tsufa.

2)Daurin kirji, sai dai in wanka kika shiga.
Ko wankan ma, make it stylish & sexy. How?
Ki kama bakin zanin duka biyu, ki daura a kijiki ki kulle, yanda zai zauna das a kirjinki yayi kuma lebatu wic looks very sexy.😃

3) Karki yarda ki tauna kashi a gaban miji.
Domin taunar kashi da shan rake kan canza yanayin mutum.
In har kina so kici kashin bari sai bakwa tare.

4) Idan ke maici ce sosai, karki bari miji ya ganki da tulin abinci a gabanki.
Yi kokari kici rabi kafin ya dawo don kinga in zaki kara kadan zaki diba.😃

5) Don Allah karki gyatsa ko tusa a gaban miji.
I beg you.

6) Karki sakace ko kaki pls.

7) Karki kuskura kiyi soshe soshe domin Bera ce kawai take wannan halin.
Allah kiyashe mu.😃

8) Karki yi karya a gaban sa.

9) Karki zagi, karki kuskura ko da kuwa an bata miki.
Musamman Ashar.
Karki ki yarda.

10) Kar ki kawo masa gulma domin zaki zubar da kimar ki a idonsa.

11) Karki yarda ya ganki da kaushi don Allah... Allah yasa mu dace da fatan zamu gyara rayuwar aure ba abin wasa bane

Copied
Babangida Ibb

SAKO ZUWA GA MAZINATA


ZUWA GA MAZINATA ::YADDA KAYI
HAKA ZA'AYI A NAKA.

Abin mamaki sai kaga mutum
musulmi ya mayar da yin zina babbar
Sana'arsa baya jin kunyar Allah balle
mutanen da take zaune a cikinsu da
yake kallon suna masa kallon mutum
mai mutunci da kima.

Dawa yawan daga cikin masu lalata
tarbiyyar yara mata bayan iyayensu
sun basu cikakkiyar kulawa da
tarbiyya addinin musulunci sai kaga
suna son su kuma su kare yayansu
da kannensu wai kada wani yayi zina
dasu!? wannan ai shine hotiho!.
Wallahi Idan kayi zina da yar wani to
ka tabbatar ko aljanu ka sanya suna
gadinta to sai anzo har cikin falon
gidanka yadda kake hutawa ayi zina
da yarka ta cikinka ko kanwarka.

Sannan Idan kana da hankali ai ya
kamata kayi tunanin wacce zakayi
zina da ita kanwar wani ce, yayar
wani ce, yar wani ce , matar wani ce,
kuma uwar wani ce fa?.
yanzu kana so ayi zina da matarka?
kana so ayi zina da yarka?
kana son ayi zina da uwaka?
kana son ayi zina da yayarka ko
kanwarka?

Tabbas na San ko shakka babu
amsarka zata zama baka so ayi
dasu !, tunda hakane to kai me yasa
zaka je ka lalata tarbiyyar da sukayi
mata?
lokacin da za kayi zina da yarinya sai
ka cire mata Riga , danuwana ka tuna
cewa mahaifinta ne ya saya mata
don kare mata mutuncinta amma kai
kuma sai ka bude mata saboda
rashin imani?.

Idan ka zama mazinaci to ka lalata
zuriyarka gaba daya domin kuwa
Annabi saw ya tabbatara mana da
cewa ana gadon zina daga wajen
mahaifi ko mahaifiya kaga kenan dole
acikin yayanka a samu mazinaci ko
mazinaciya ko baka so kuwa kuma
komai tsarin daka bayar kuwa.
Sannan ka gane zina bata buya ko
Ba a garinku kakayi ba indai kai
mazinaci ne wallahi sai Allah ya tona
maka asiri kowa ya gane halinka.

Ni Sirajoa Isah Yunusa ina rokon
Allah da dukkanin sunayensa
kyawawa ya karemu daga fada cikin
wannan musifar gaba dayan wadanda
suka shiga cikinta kuma manya da
yara Ubangiji idan masu shiryuwane
Ka shiryesu Idan Ba masu shiryuwa
bane Allah ka nisanta su daga
garemu da yayanmu da kannenmu da
matanmu kamar yadda ka nisanta
gabas da yammma.

 

Thursday, April 16, 2020

TARBIYYAR YARA



TARBIYYAR YARA A MUSULUNCI. //1
TARBIYYA hakkine da Allah (SWT) ya wajabtawa Iyaye suyi ga 'ya'yansu, kamar yadda ya wajabtawa 'ya'ya yin biyayya ga iyayensu.
Kamar yadda muka sani, 'ya'ya kyautace (Ni'imace) daga Allah da yake bayar da ita ga wanda yaga dama, kuma Amanace da Allah ya dankata a hannun iyaye. Sabida haka Iyayen da suka kyautata wajen tarbiyyantar 'ya'yansu da ladabtar dasu bisa koyarwar Musulunci, to sun sauke wannan amanar, Wadanda kuma suka yi sakaci kuma suka takaita wajen yi musu tarbiyya to sun tozarta wannan Amanar.
Allah Ta'ala yace: " Ya ku wadanda su kayi imani, ku tsare kawunanku da iyalanku daga wuta, wacce mutane da duwatsu ne makamashinta... "
(Tahrim: 6).
Annabi (SAW) yana cewa a wani hadisi:
" Dukkanninku masu kiwone kuma ababan tambayane dangane da kiwon da aka baku, shugaba me kiwone (dangane ga talakawansa) kuma abin tambayane dangane da kiwon da aka bashi, mutum me kiwone dangane ga iyalinsa kuma abin tambayane dangane da kiwon da aka bashi."
Bukhari da Muslim.
Akwai wasu hanyoyi wadanda idan muka bisu zasu taimaka mana da yardar Allah wajen Tarbiyyar 'yayanmu, daga cikinsu akwai:
1. MU ZABAWA 'YA'YANMU UWA TA GARI.
Auren mace tagari muhimmin lamarine dake taimakawa wajen tarbiyyar 'ya'ya, domin uwa ita ce makaranta ta farko da yaro ke daukar darasi a cikinta, kuma halaye da dabi'un uwa suna tasiri matuka ga 'ya'yanta, sabida hakane shari'a ta kwadaitar damu wajen auren mace tagari ma'abociyar addini.
Annabi (SAW) yana cewa: " Ana auren mace sabida abubuwa guda 4; dukiyarta, da kyawunta, da daukakarta, da addininta. ka zabi ma'abociyar addini, sai hannunka yayi albarka."
Bukhari da Muslim.
Abu ne mai muhimmanci ga wanda yake da niyyar yin aure ya dage da addu'a akan Allah ya azurtashi da samun mace tagari, kuma yayi "istikhara" wato neman shawarar (zabin) Allah kafin auren, ya kuma nemi shawarar bayin Allah mutanen kirki, sannan yayi kokari wajen yin bincike akan nagartar yarinyar da kuma iyayenta, ya kuma fawwala al'amuransa zuwa ga Allah SWT.
Sannan kuma ya zama wajibi abi hanyoyin da Shari'a ta tsara wajen neman aure, kuma a nisanci sabawa Allah da sunan murna ko farinciki a yayin aure, wannan zai sa Allah Ta'ala ya sanya Albarka a cikin auren da kuma zuriyar da za a samu ta dalilin wannan auren.
2. ROKON ALLAH YA BAKA ZURRIYYA TA GARI.
Wannan dabi'ace ta Annabawa da Manzanni da bayin Allah salihai. Kamar yadda Allah ya bamu labari a kissar Annabi Zakariyya (AS), yake cewa: " A yayin nan Annabi Zakariyya ya roki Ubangijinsa, yace: ya Ubangiji ka bani kyauta daga gareka ta zuriyya tsarkakakkiya, hakika kai mai amsar addu'ane."
(Ali-Imran: 38)
A wata ayar kuma Allah ya bamu labarin salihan bayinsa, daga cikin siffofinsu suna addu'ar Allah ya basu mata da 'ya'ya nagari, yake cewa:
" Wadannan da suke cewa ya Ubangijinmu ka bamu kyauta daga matayenmu da zuriyyarmu abinda idanuwanmu za suyi sanyi dasu, kuma ka sanyamu mu zama shugabanni ga masu tsoron Allah."
(Al-furqan: 74)
Wannan ya nuna mana muhimmancin addu'a da rokon Allah wajen samun 'ya'ya nagari kasancewar har Annabawan Allah da Salihai sun yi irin wannan addu'ar.
Allah ya bamu ikon yiwa 'ya'yayenmu tarbiyya da ladabdar dasu bisa koyarwar Kur'ani da Sunnah,

Thursday, March 26, 2020

GANIN GASHIN CORONA VIRUS




GASHIN_CORONAVIRUS..
ALHAMDULILLAH
Na kammala dukkanin binciken da zanyi akan wannan GASHIN... Kuma zahiri Naga GASHIN agurare MAban-banta....
A'INA NAGA GASHIN KUMA MAI NE NE SHAIDA.!
Dafarko na Dauko ALQUR'ANI NAH ,na duba bangani ba, Na sake dauko wani ALQUR'ANI NAH Wanda bancika amfani dashi ba....
Ina daukowa Naduba suratul Baqara banganiba har qarshe Bangani ba...
Wanda a yanda ake ya'da labarin a suratul baqara kawai ake gani....
Na cigaba da budewa Allah cikin ikonsa Na duba suratul Al-imrana, na samu GASHIN ,na duba nisa'i na samu, daga nan WALLAHI kusan ko wace sura na bude sai na samu....
..
..Dahaka ne nadinga dauka daya bayan daya INA taarawa ,wani na iya dauka ,wani Kuma inna dauko sai ya fadi saboda sirantar sa..
SHIN ACIKIN ALQUR'ANI KAWAI AKE GANIN GASHIN KO HAR A WASU LITTAFAN...?
Nayi mamaki da afkuwar hakan ainun....
Sai nayi wani tunani nace bari na duba littafan BOKO... Irinsu Textbooks da Novel da sauran makamantan su.....
Na je na dauko wani tsohon littafi na,Wanda aka rubuta shi,Akan tarihin Samun 'YANCIN NIGERIA ,Na mahaifi NAH na duba Shima na samu ziri daya nagashin Wanda na iya daukowa...sauran sunyi siranta dayawa bazasu dauku ba.....!
SHIN WANNAN GASHIN YAYA KALARSA TAKE..?!
GASHIN zaku sameshi kamar zare ,siriri ,BAQI DA FARI AKWAI KUMA JAA ...
KAMAR YANDA NAGA RUBUTUN WANI DAN UWA YA TABBATARDA CEWAR WANNAN ZAREN ZA'A IYA SAMUNSHI AKOWANE IRIN LITTAFI....DALILIN SAMUWAR SA ,DAGA PUBLISHING COMPANY NE(MA MAIKATAR BUGA LITTAFAI)
SUBHANALLAH..!!!
SHINE WASU 6ARA GURBIN MUSULMI SUKE AMFANI DA WANNAN DAMAR WAJEN KIRKIRAWA ANNABI S.A.W QARYA...
ANNABI S.A.W "YACE DUK WANDA YAYI MINI QARYA DA GANGAR TO YA TATTALI MAZAUNINSA A WUTA...
*BAYAN HAKA GA WULAQANTA LITTAFIN ALLAH.....
Allah kadai yasan adadin mutanen dasuke da janaba ko Haida ko qananun yara marasa tsarki suka dinga daukar ALQUR'ANI..
*AMADADIN A KOMA GA ALLAH AMMA SAI AKE QOQARIN JANYO MANA WATA MASIFAR...
Wal'iyazuBilLAH....
ALLAH YAMANA TSARI DAGA 'YAN DANFARAR IMANI...
ALLAH KADAI YASAN ADADIN MUTANEN DA SUKA JIQA ZARE (DASUNAN GASHI) SUKASHA...
MUTANE IDON SU YARUFE SUNA TUNANIN AKWAI WANDA YA ISA YADAUKE MANA WANNAN MUSIBAR TA CORONAVIRUS BAYAGA ALLAH...?
KO KUN MANTA SHEKARU DASUKA SHUDE...
AKACE MANA ANA GANIN DODON BANGO...
ALLAH YAJIQAN WANI MALAMIN AHLUSSUNAH BADAN YA MUTUBA....
Alokacin muna cikin uqubar wani shugaba,MALAMIN YACE " tunda ana ganin shi shi DODON bangon mai yasa baza'a fa'da masa ba yazo ya murqushe mana wannan azzalumim shugaban In gaskiya ne...
HAka wata yarinya a unguwar mu ,taxi ta qoshi yayi barci ta farka wai sai kawai taga DODON BANGO acikin dakinta....
MUTANE NATA tururuwar zuwa gani ....
Alokacin wasu suce sun ganshi bakai at are dashi ajikin BANGO wasu suce sunganshi complete da sanda.... Alokacin idan mutum bai samu ikon ganinsa ba sai ace wai bashida rabo....
Hatta 'YAN jarida saida suka kawo mata ziyara alokacin.....
...BAyan wasu kwanaki Ashe wai TAMBOTSAN samankanta ne keyi mata gizo..da sauran 6attatun mutanenta.....
HAKA AKAYI ASHEKARUN BAYA DASUKA SHU'DE AKAN EBOLA...
Aka dinga YA'DA jita-jitan shan ruwan gishiri da kuma wanka dashi....
MUTANE suka manta Allah acikin ZUKATANSU....
Sanadin shan ruwan gishiri yayi sanadiyyar Mutuwar MUTANE da da-ma wasu kuma sukamkamu da cututtuka....
Da aka tsananta bincike. Ashe wai PASTOR ne yayi MAFARKI......
....WANNAN KARON KUMA SAI AKAZO DA SABON SALON YAUDARA DAKUMA DAMFARAR IMANI.....
Wanda WALLAHI MUTANE dayawa suntafi ahakan..
..★TO BARA KUJI KU MASU SHAN RUWAN GASHI(ZARE) IDAN SANADIN KAMUWA DA WASU CUTUKAN NE YAZO ALLAH YABADA SA'A★
YAYIN DA MUTANE SUKA MANTA ALLAH AZUKATANSU SAI ALLAH YA BARSU DA IYA WARSU...
ALLAH YASA MUTANE SU HANKALTA...!
YAA! UBANGIJIN MU KARKA KA-MAMU DA LAIFINDA WASU WAWAYE DAGA CIKIN MU SUKE AIKATAWA....
#GA_HUJJA_NAN_NAKAWO_MANA_AWANNAN_HOTON...
#KUNSAN_ITA_HUJJA_ #TAKOBIN_AHLUSSUN_NAH
Safeeyyah Suleiman Umar