Sunday, December 29, 2019

FA'IDODIN DA SUKE CIKIN YIN AURE




FA'IDODIN DA SUKE CIKIN YIN AURE
*************************************
Fa'idodin da suke cikin aure ba zasu
Kididdigu ba. Amma ga wasu ka'dan
daga ciki zamu lissafo kamar haka:
1. Yin aure biyayya ne ga Umurnin
Allah da Manzonsa.
2. Yin aure yana sanya Manzon Allah
(saww) farin ciki aranar lahira. Yace :
"Kuyi aure ku hayayyafa. Domin ni
zanyi ma sauran al'ummomi alfahari
daku aranar Alkiyamah".
3. Ta dalilin aure zaka samu wanda
Zai fito ta jikinka, har ya girma yana
Kalmar Shahada!! "LA ILAHA ILLAL
LAHU MUHAMMADUR RASULALLAHI".
4. Ta dalilin aure ne zaka samu
Zuriyar da zasu yi maka addu'a
bayan rasuwarka. Wannan yana daga
cikin ayyukan da ladansu ba zai
yanke ba har abada.
5. Yin aure ya kan zama dalilin
runtsewar idanun mutum daga kalle
kallen Haramun, sannan ya kare masa
al'aurarsa daga Zina.
6. Ta dalilin aure ne zaka samu
damar taimaka ma 'Yar uwarka
Musulma, ka aureta, ka Kiyayeta
kenan daga Zina.
7. Ta dalilin aure ne zaka samu cikar
addininka, da ninkawar ladanka fiye
da wanda bashu da aure.
8. Ta dalilin aure ne zaka samu ladan
ciyarwa da Matarka, da daukar
nauyinta, da ladan samar mata da
Mazaunin da zata rayu.
9. Ta dalilin aure ne zaka samu
damar Qara yawan Musulman duniya
ta hanyar haihuwar da zaka samu.
10. Ta dalilin aure ne zaka samu
damar Karkatar da himmarka daga
kan neman biyan bukatarka ta hanyar
haram izuwa ga hanyar halal. Da
kuma samun ladan saduwa da
iyalanka.
11. Zaka samu lada mai girma sosai
idan Har Allah ya azurtaka da 'Ya'ya
mata guda biyu, kumq kayi hakuri
dasu ka kyautata musu, ka kyautata
tarbiyyarsu, Su zasu zama
Garkuwarka daga shiga wuta.
12. Idan ka har 'Ya'yanka guda biyu
suka rasu, kuma kayi hakuri, to Allah
zai shigar dakai Aljannah saboda
wannan.
13. Ta dalilin aure zaka samu
Qaruwar mutuncinka da darajarka
acikin al'ummah. Ka shiga sahun
mutanen da zasu iya jagorantar
lamuran rayuwar al'ummah.
14. Ta dalilin aure ne zaka Samu
Taimakon Allah cikin al'amarinka.
Kamar yadda Manzon Allah (saww)
yake cewa: "
MUTUM UKU, HAKKI NE
AKAN ALLAH YA TAIMAKESU. 1.
WANDA ZAI YU AURE DON NUFIN
KAME MUTUNCINSA. 2. BAWA
WANDA YAKE NEMAN 'YANCINSA
SABODA YA SAMU DAIDAITUWA
(ACIKIN ADDINI) 3. MUJAHIDI (MAI
YAKIN DAUKAKA ADDININ ALLAH

No comments:

Post a Comment