Sunday, December 29, 2019

BABBAR MAGANA:



BABBAR MAGANA:
Ranar Lahira Allah yana cewa:
(Ya ku wadanda suka yi imani, ku kiyaye dokokin Allah, kowane mai rai ya dubi abin da ya aikata domin gobe (lahira)…) [Al-Hashri, aya ta 18].
1. Mutuwa ba ita ce karshe ba. Mutuwa mafarin wata rayuwa ce mai tsawon gaske, mai ciki da dadi ko wahala, mai kunshe da farin ciki ko bakin ciki. Duk mai kokwanto game da rayuwar lahira mahaukaci ne ba mai hankali ba.
2. Rayuwarmu a nan duniya tana cike da zalunci da ta'addanci da rashin gaskiya da miyagun ayyuka. An mayar da karya ita ce mafita, yaudara kuma ita ce wayo munafurci kuma ya zamawayewa.
3. A rayuwarmu a yau muna ganin ana hukunta marar laifi a kyale masu laifuka, ana kuma wulakanta mai mutunci sannan a karrama fitsararre. Don haka idan har mun yarda da cewa Allah adalin Sarki ne, to babu makawa dole ne mu yi imani da samuwar wata rayuwa bayan wannan ta duniya da muke ciki, watau rayuwa wadda a cikinta ne Allah zai mayar wa kowane mai hakki hakkinsa, ya hukunta duk wani mai laifi gwargwadon laifinsa. Duk wani mai hankali da ya san ya kamata dole ne ya yarda da haka.
4. Yarda da lahira da imani da sakamakon cikinta ne kadai zai hana wa dan'adam zaluntar dan'uwansa, zai kuma kara wa mutumin kirki kwarin gwiwar aikata ayyukan alheri,domin yana da tabbacin cewa zai ga kyakkyawan sakamakon aikinsa.
5. Ashe bai kyautu mu ci gaba da tunatar da junanmu wannan babbar magana ba

FALALAR RAKA'ATAYIL FAJRI



FALALAR RAKA'ATAYIL FAJRI
*******************************
Raka'atayil Fajri : Sune raka'o'in nan guda biyu na nafila wadanda ake yi bayan Hudowar Alfijir, kafin sallar Asubahi.
Wannan sallar tana da inganci sosai. Domin Annabi (saww) ya bata muhimmanci. Ya kasance yana yinta aduk halin da yake ciki. Koda awajen tafiya, ko azaman gida.
Malamai sun ce ana karanta Fatiha ne da Qul Ya ayyuhal Kafirun, da kuma fatiha da Qul Huwal-Lahu acikinta. KUMA ana yinta ne aboye. (wato yana yin karatunta a sirrance).
Daga cikin falalarta, Sayyiduna Abdullahi bn Umar (rta) ya ruwaito cewa wani mutum ya tambayi Manzon Allah (sallal Laahu alaihi wa aalihi wa sallam) cewa :
"Ya Rasulallahi ina so ka nuna min wani aiki wanda Allah zai amfanar Dani saboda shi".
Sai Annabi (saww) yace masa "KA KULA DA RAKA'ATAYIL FAJRI DOMIN ACIKINTA AKWAI FIFIKO (WATO FALALA)".
(Tabaraniy ne ya ruwaitoshi).
Acikin wata ruwayar kuma Abdullahi bn Umar (ra) yace "Naji Manzon Allah (saww) yana cewa :
"KAR KU BAR YIN RAKA'O'IN NAN GUDA BIYU WADANDA AKEYI KAFIN SALLAR ASUBA. DOMIN ACIKINSU AKWAI ABABEN KWADAYI".
Domin cikar fa'idah ma, ga wani Sahihin hadisin wanda Imamu Muslim ya ruwaito daga Nana A'ishah (ra) ita kuma daga Manzon Allah (saww) yana cewa:
"RAKA'O'I BIYUN ALFIJIR, SUN FI DUNIYA DA ABIN CIKINTA".
Don haka 'yan uwa bai kamata mu rika barin wannan garabasar tana wucemu ba.
Da yawan Matasa Wasu basu yinta. Dama basu kwanciya da wuri, shi yasa suke makara. Kuma da zarar sun tashi sai su sallaci Asubah, ita kuma su kyaleka.
To lallai rashin yin RAKA'ATAYIL FAJRI ba Qaramar Asara bace agareka ya kai Musulmi!
Wannan asarar tafi asarar Biliyoyin Nairori. Domin kuwa Annabi (saww) yace TAFI DUNIYA DA ABIN CIKINTA. Don haka idan baka yita ba, kamar kayi asarar dukiyar dake cikin duniyar nan ne. Ko kuma fiye da haka.
Na san yanzu wani zai ce "Shin zan iya yinta koda bayan Sallar Asubah ne?".
AMSA : A'a. Ana yinta ne kafin sallar Asubah. Domin bai halatta kayi sallar nafila bayan kayi ta Asubahi ba. Har sai bayan fitowar rana.
Hujjah anan ita ce Sahihin hadisin da Imamul Bukhariy da Muslim suka ruwaito daga Abu Sa'eed Alkhudriy (ra) daga Manzon Allah (saww) yana cewa:
"BABU SALLAH (NAFILAH) BAYAN SALLAR LA'ASAR HAR SAI RANA TA FADI. KUMA BABU SALLAH BAYAN SALLAR ASUBAH HAR SAI RANA TA BULLO".
Wani Sahabi mai suna Amru bn Abisata (ra) yace "Ya Rasulallahi bani labari mana game da sallah".
Sai yace masa "KA SALLACI ASUBAH SANNAN KA JANYE DAGA YIN SALLAH HAR SAI RANA TA FITO TAYI SAMA.....".
Imamu Ahmad da Muslim ne suka ruwaitoshi).
Mafiya yawan Jamhurin Malamai suna ganin halaccin yin ramukon sallah akowanne lokaci, koda bayan Sallar Asubah din ne. Amma banda nafila.
Saboda hadisin da Imamul Bukhariy da Muslim suka ruwaito daga Manzon Allah (saww) yana cewa:
"DUK WANDA YA MANTA DA WATA SALLAH (TA FARILLAH KENAN) TO YA SALLACETA IDAN YA TUNA".
Amma yin nafila bayan Sallar Asubah, mafiya yawan Sahabbai duk sun karhanta yin haka. Kamar Irin su Sayyiduna Aliyu Bn Abi Talib. Da Ibnu Mas'ud da Zaidu bn Thabit da Abu Hurairah da Ibnu Umara (Allah shi yarda dasu baki dayansu).
Sayyiduna Umar kuwa, ya kasance yakan bugi mutum idan ya ganshi yana yin nafila a irin wadannan lokutan.
Hakanan Sayyiduna Khalid bn Waleed (ra) Shima yakan bugi masu yin hakan. (Wato masu yin nafila alokutan da aka hana).
Duk da cewa akwai Maluman da suka halatta yinta bayan an sallaci Asubah, wai saboda Hadisin wani mutum wanda ya tashi bayan Sallar Asubah yana yinta amma Annabi (saww) bai ce masa komai ba. To amma gaskiya hujjarsu bata kai wannan din Qarfi ba. ta kowacce fuska.
Saboda wannan haka Annabi (saww) yake yi, Haka Khalifofinsa gaba daya suke yi. Hakanan duk manyan Sahabbansa wadanda aka riko sunnah daga garesu duk suna yinta ne kafin sallar Asubahi (Ba bayanta ba) Haka kuma, dukkan Maluman Mazahib din nan guda hudu.
Anan zan tsaya, sai wani lokacin kuma in sha Allahu. Da fatan Allah shi amfanemu da abinda muka karanta.
An gabatar da karatun a Zauren Fiqhu -3 (28-02-2016).
DAGA ZAUREN FIQHU WHATSAPP. (07064213990).

DALILAI 11 DAKE JAWO ARZIKI



DALILAI 11 DAKE JAWO ARZIKI. DAGA KUR'ANI DA HADIS.
1 Ilimi da kwazon aiki da shi.
2 Dogoro ga Allah ta'ala kawai. suratul dalaki 3
3 Istigifari suratul nuh. 10-12 4 Tuba na gaskiya suratul hud 3
5 Tsoton Allah S.W.T. suratul.A'Araf 96
6 Anbaton Allah a Zuci da baki da gabbai. suratul daha 124
7 Ciyarwa da taimakon na kasa. suratul saba'I. 39
8 Sada zumunta. Buhari, Muslum, Nasaiy, Ibn Majah, Al Imam Ahmad da Abu Dauda
9 Addu'a , Allah ina neman tsarinka daga talauci da kafirci.
10 Taimakawa daliban Ilimi. Attirmiziy
11 Godiya ga Allah ta'ala. suratul Ibrahim 7

KUSKUREN DA MATA SUKE AFKAWA YAYIN 'DAUKEWAR JININ HAILA


KUSKUREN DA MATA SUKE AFKAWA YAYIN 'DAUKEWAR JININ HAILA*
_______________
Mafi yawan mata idan jinin al'ada ya 'Dauke musu suna jinkirta wanka da niyar ko jinin zai Qara dawowa.
Wasu sukan Qara kwana 'Daya zuwa biyu bayan haila ya 'Dauke.
Wasu kuma idan suka ga alama guda 'Daya na 'Daukewar jinin, sai suce zasu jinkirta wanka domin su jira zuwan sauran alamomin. Misali: Mace taaga bushewar gaba amma bata ga Farin ruwa ba, wanda ake kiransa da larabci (قصة البيضاء), daga nan sai tace bari ta bari sai farin ruwa yazo sannan tayi wanka ta cigaba da sallah da azumi.
Duka Wannan kuskure ne babba
Abinda yake wajibi shine: Da zarar taga jini ya tsaya ko taga alamomin Daukewar Jinin haila, toh wajibi ne tayi wanka nan take ta cigaba da ibadar ta. Qin yin wanka har lokacin sallah ya wuce babban zunubi ne.
Allaah ya tanadi Azaba mai tsanani ga masu wasa da sallah.
Allaah yace:-
" ﻓَﻮَﻳْﻞٌ ﻟِﻠْﻤُﺼَﻠِّﻴﻦَ ‏(4 ‏) ﺍﻟَّﺬِﻳﻦَ ﻫُﻢْ ﻋَﻦْ ﺻَﻠَﺎﺗِﻬِﻢْ ﺳَﺎﻫُﻮﻥَ "
{ﺍﻟﻤﺎﻋﻮﻥ : 5-4 }
Allaah ya qara da cewa:-
" ﻓَﺨَﻠَﻒَ ﻣِﻦْ ﺑَﻌْﺪِﻫِﻢْ ﺧَﻠْﻒٌ ﺃَﺿَﺎﻋُﻮﺍ ﺍﻟﺼَّﻠَﺎﺓَ ﻭَﺍﺗَّﺒَﻌُﻮﺍ ﺍﻟﺸَّﻬَﻮَﺍﺕِ ﻓَﺴَﻮْﻑَ ﻳَﻠْﻘَﻮْﻥَ ﻏَﻴًّﺎ "
{ﻣﺮﻳﻢ : 59 }
...... Da ayoyi masu yawa cikin al-Qur'ani.
daga lokacin da jini ya 'Dauke, ibada ya wajaba ga mace.
idan mace ta jinkirta sallah toh sai ta rama su bayan tayi wanka, sannan tayi istigfarin jinkirin sallah
*_Idan kin karanta kiyi Qoqarin turawa yar uwarki musulma zaki samu lada in shaa Allaah_______

FA'IDODIN DA SUKE CIKIN YIN AURE




FA'IDODIN DA SUKE CIKIN YIN AURE
*************************************
Fa'idodin da suke cikin aure ba zasu
Kididdigu ba. Amma ga wasu ka'dan
daga ciki zamu lissafo kamar haka:
1. Yin aure biyayya ne ga Umurnin
Allah da Manzonsa.
2. Yin aure yana sanya Manzon Allah
(saww) farin ciki aranar lahira. Yace :
"Kuyi aure ku hayayyafa. Domin ni
zanyi ma sauran al'ummomi alfahari
daku aranar Alkiyamah".
3. Ta dalilin aure zaka samu wanda
Zai fito ta jikinka, har ya girma yana
Kalmar Shahada!! "LA ILAHA ILLAL
LAHU MUHAMMADUR RASULALLAHI".
4. Ta dalilin aure ne zaka samu
Zuriyar da zasu yi maka addu'a
bayan rasuwarka. Wannan yana daga
cikin ayyukan da ladansu ba zai
yanke ba har abada.
5. Yin aure ya kan zama dalilin
runtsewar idanun mutum daga kalle
kallen Haramun, sannan ya kare masa
al'aurarsa daga Zina.
6. Ta dalilin aure ne zaka samu
damar taimaka ma 'Yar uwarka
Musulma, ka aureta, ka Kiyayeta
kenan daga Zina.
7. Ta dalilin aure ne zaka samu cikar
addininka, da ninkawar ladanka fiye
da wanda bashu da aure.
8. Ta dalilin aure ne zaka samu ladan
ciyarwa da Matarka, da daukar
nauyinta, da ladan samar mata da
Mazaunin da zata rayu.
9. Ta dalilin aure ne zaka samu
damar Qara yawan Musulman duniya
ta hanyar haihuwar da zaka samu.
10. Ta dalilin aure ne zaka samu
damar Karkatar da himmarka daga
kan neman biyan bukatarka ta hanyar
haram izuwa ga hanyar halal. Da
kuma samun ladan saduwa da
iyalanka.
11. Zaka samu lada mai girma sosai
idan Har Allah ya azurtaka da 'Ya'ya
mata guda biyu, kumq kayi hakuri
dasu ka kyautata musu, ka kyautata
tarbiyyarsu, Su zasu zama
Garkuwarka daga shiga wuta.
12. Idan ka har 'Ya'yanka guda biyu
suka rasu, kuma kayi hakuri, to Allah
zai shigar dakai Aljannah saboda
wannan.
13. Ta dalilin aure zaka samu
Qaruwar mutuncinka da darajarka
acikin al'ummah. Ka shiga sahun
mutanen da zasu iya jagorantar
lamuran rayuwar al'ummah.
14. Ta dalilin aure ne zaka Samu
Taimakon Allah cikin al'amarinka.
Kamar yadda Manzon Allah (saww)
yake cewa: "
MUTUM UKU, HAKKI NE
AKAN ALLAH YA TAIMAKESU. 1.
WANDA ZAI YU AURE DON NUFIN
KAME MUTUNCINSA. 2. BAWA
WANDA YAKE NEMAN 'YANCINSA
SABODA YA SAMU DAIDAITUWA
(ACIKIN ADDINI) 3. MUJAHIDI (MAI
YAKIN DAUKAKA ADDININ ALLAH

MARRIAGE TO MORETHAN ONE WIFE



MARRIAGE TO MORETHAN ONE WIFE
------------
*Quran' chapter 4 verse 3 (suratu-nisai)*
.........فانكحواماطاب لكم من النساء مثن وثلث وربع........
*.............marry 2, or 3, or 4. But if u are are afraid of justice amongst ur wives,,,then marry one.*
--------------
*JUSTICE AMONG WIVES*
*Qur'an chapter 4 verse 128*
ولن تستطيعواان تتعدلوا بين النساءولوحرصتم فلاتميلواكل الميل...........
*U will not be able to do justice (( interms of LOVE//FEELINGS ))among ur wives, even if u strive to do so. But do not turn completely (openly) for only one of them.............*
++++++++++
*Justice in this verse is not interms of LOVE but interms of shelter,feeding, dresses,children etc etc etc.*
+++++++++
*DID U EVER THINK OF THESE?*
*1. Birth rate statistics shows dat 65% of birth are girls and only 35% are boys.*
*2. Did u ever go to schools? ( primary,secondary,tertiary ),,the ratio of male : female is approximately 35:65*
*3. Death rate statistics shows dat male 60%, female 40%. Accident claims more male than female due to struggle for survival. Plus other ways.*
*4. Did u ever compare the physical outlook of a man of 45 years with a female of 45 years? Who among them look seriously younger?*
+++++++++
*I remember hadith of d prophet Muhammad SAW*
لايومن اهدكم حتى يحب لاخه ما يحب النغسه
*U are not a believer, EXCEPT u love for ur fellow what u love for Urself*
++++++++
*DISTURBING QUESTIONS*
*1. What will happen to the remaining population of females, if every man should marry only one wife?*
*2. If u give birth to 5 female children, and u also have very plenty sisters who are yet to marry. WHO WILL MARRY them.*
*3. If a woman got married to a man at d age say 20-25. And d husband eventually died 5years after their marriage. Is that how d woman will die without remarriage?*
😳😳😳😳
😭😭😭😭
*My brother//sister inslam,,, we should fear Allah and love for others what we love for ourselves.*
+++++++
*U can not stick to only one wife when u are blessed to some extent to marry 2, or 3, or 4,,, OR WOMEN THAT ARE TROUBLING THIER HUSBAND NOT TO MARRY ANOTHER WIFE,,,and yet u expect ur daughters to get married with ease.*

MACE MAI WUYAR SAMU A YAU



MACE MAI WUYAR SAMU A YAU
__________________________________
Ya kamata mu sani cewa mace daya ce a duniya take da wuyar samu, amma idan ka samu irinta, kada ka kuskura ka rabu da ita. Ya halatta ka auri mace fiye da daya, amma ka sani, mace daya ce kawai, ta ke yin tasiri a rayuwa, wacce ranka kullum zai kasance a kanta.
Babbar tambaya a nan ita ce, wacece wannan dayar? Ita ce wadda duk da namiji yake muradin samu a rayuwarsa, Ita ce wadda ke koyi da rayuwar shugabar matan duniya kuma diya ga Rasulallahi (SAW), wato Nana Fatima (Allah Ya kara mata yarda).
Haka kuma ita ce wadda kowace mace take fata ta zama.
Ga siffofinta guda goma, kamar.
haka:
1. Matar da ta yarda ita mace ce, don haka ta tanadi duk abin da ake bukata a wajan mace.
2. Mace mai hikma da azanci, wacce ta karanci mijinta da kyau, kuma take kaucewa duk abin da
zai haddasa matsala a tsakaninsu.
3. Mace mai taushin hali da nutsuwa, wacce miji yake jin nutsuwa, idan yana tare da ita.
4. Mace da kudi bai dame ta ba, ita mijinta kawai take so, ko da akwai ko babu.
5. Mace mai hakuri da juriya, babu gunaguni, babu mita, da kai kara ga iyaye ko kawaye.
6. Macen da ta dauki kanta likita, mijinta mara lafiya, domin ya sami kulawa, ta musamman da.
riritawa.
7. Mace mai saurin daukar ishara, tana gane shiru da magana, da motsi da yanayin shigowa da
fita, samu da rashi da kuma yanayin da ake ciki a duniya ko a gari.
8. Mace mai sakakkiyar zuciya, mara kulli da ramuwa.
9. Mace mai karawa miji kuzari da karfin hali, a kan kyawawan manufofinsa.
10. Mace mai rikon amanar aure, da soyayya ga mijinta kawai.
Fatanmu ubangiji yasa mudace da mata na Kwarai.